in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bai kamata kasashen ketare su tsoma baki cikin harkokin Hong Kong ba
2014-06-01 17:15:12 cri
Jami'in musamman na ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin a yankin Hong Kong dake nan kasar Sin Mr. Song Zhe, ya ce harkar bunkasuwar siyasar yankin Hong Kong, harka ce ta cikin gidan Sin, wadda ko kadan bai kamata kasashen ketare su rika tsoma baki cikin ta ba.

Mr. Song wanda ya bayyana hakan yayin tattaunawarsa da shugabar ofishin kansula na kasar Burtaniya dake yankin na Hong Kong Caroline Elizabeth Wilson, ya yi fatan kasar Burtaniya za ta mai da hankali kan kiyaye dangantakar dake tsakaninta da Sin, ta kuma yi kokarin kiyaye yanayin zaman karko da wadatar yankin.

Har ila yau wata sanarwa daga shafin yanar gizon ofishin babban jami'an musamman da ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Sin ta aike zuwa yankin na Hong Kong, ta ce, ganawar da Mr. Song ya yi da Wilson a ranar 29 ga watan Mayu, ta karkata ne ga shawarta batutuwa da suka shafi dangantakar kasashen biyu, da yanayin siyasa, da tattalin arzikin yankin na Hong Kong.

Kaza lika Mr. Song ya jaddada matsayin gwamnatin kasar Sin, dangane da ka'idojin bunkasa harkokin yankin na Hong Kong. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China