in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bayyana dacewar gudanar zaben kujerar shugabancin kula da harkokin Hong Kong bisa dokoki
2014-08-31 20:13:27 cri
A Lahadin nan 31 ga wata ne shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasa ta Sin Zhang Dejiang, ya bayyana kudurorin da zaunannen kwamitin ya cimma yayin zamansa na wannan karo. Kudurorin dake da muhimmiyar ma'ana da suka kunshi raya dimokuradiyya a yankin musamman na Hong Kong, da kuma batun gudanar da zaben kujerar shugabancin kula da harkokin yankin a shekarar 2017 bisa dokokin kasa yadda ya kamata

Mr. Zhang ya bayyana hakan ne dai ya yin bikin rufewar taro karo na 10 na zaunannen kwamitin karo na 12. Kaza lika da yammacin wannan rana, an zartas da kudurorin da suka shafi harkokin zaben shugaba mai kula da harkokin yankin musamman na Hong Kong, da kuma yadda za a iya kai ga kafa majalisar dokoki a yankin a shekarar 2016, a taron zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasa ta Sin.

Bugu da kari, Zhang Dejiang ya ce, goyon bayan yankin musamman na Hong Kong bisa kudurin neman bunkasuwarsa karkashin babbar dokar kasa ya dace da tsarin dimokuradiyyar yankin, kuma hakan ne matsayin da gwamantin kasar Sin ke kai a ko da yaushe. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China