in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bangarori daban daban na Hongkong sun yi maraba da kudurin da NPC ya tsaida game da zaben babban jami'in yankin na musmaman
2014-09-01 15:59:20 cri
A ranar 31 ga watan Agusta ne, zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ya tsaida kuduri game da zaben kantoman yankin musamman na Hongkong da dabarar kafa majalisar dokoki a shekarar 2016, inda bangarori daban daban da ke yankin suka bayar da ra'ayoyi da sanarwar yin maraba da kudurin a wannan rana.

Kantoman yankin musamman na Hongkong Leung Chunying ya bayyana a yammacin ranar 31 ga watan Agusta cewa, jami'an da ke kula da harkokin yankin da membobin majalisar da ba jami'ai ba sun nuna goyon baya ga kudurin da zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ya yanke.

Yanzu kantoman da gwamnatin yankinsa za su yi kokarin aiwatar da kudurin don cimma burin zaben babban jami'in yankin na musamman wanda jama'a fiye da miliyan 5 za su zaba.

Bangaren 'yan kasuwa shi ma ya yi maraba da wannan kuduri.

Shugaban babbar kungiyar 'yan kasuwa ta yankin Hongkong YK Pang ya bayyana cewa, zaben wanda zai shugabanci harkokin yankin na Hong Kong shi ne burin jama'ar yankin a zaben da za a yi a shekarar 2017 don zaben babban jami'in yankin na musamman dake dacewa da ra'ayoyin jama'ar yankin, wannan zai kasance abu mai muhimanci a tarihin yankin.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China