in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya taya Masoum murnar lashe zaben shugaban Iraki
2014-07-28 20:33:29 cri
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya taya Faud Masoum murna bisa zabensa da aka yi a matsayin shugaban kasar Iraki.

Shugaba Xi wanda ya bayyana hakan cikin sakon da ya aika wa sabon shugaban ya ce, a shirye yake ya hana kai da sabon shugaban don karfafa dangantakar da ke tsakanin Sin da kasar Iraki.

Ya kuma bayyana cewa, kasar Sin tana goyon bayan shirin kasar na sassanta bangarorin siyasa da sake farfado da tattalin arzikin kasar, tare da imanin cewa, al'ummar kasar Iraki za su iya magance matsalolin da suke fuskanta sannan za su maido da zaman lafiya da ci gaba cikin hanzari.

A ranar Alhamis ne 'yan majalisar dokokin kasar ta Iraki suka zabi Masoum a matsayin sabon shugaban kasar, matakin da ke nuna muhimmin ci gaban da aka samu na kafa sabuwar gwamnati a kasar. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China