in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar SADC ba zata cimma dokar hana tafiya ba dalilin cutar Ebola
2014-08-19 10:42:43 cri

Babban sakataren zartaswa na kungiyar ci-gaban gabashin Afrika SADC, Stergomena Lawrence Tax, ta bayyana a ranar Litinin cewa kasashe mambobin goma sha biyar na gamayyar SADC ba za su amince da hana tafiya ba bisa dalilin cewa wasu daga kasashen yammacin Afrika suna fama da cutar Ebola.

Kungiyar SADC ba za ta hana masu tafiya ba kana ba za ta takaita zirga-zirgar jiragen sama dake fitowa daga kasashen da cutar ta shafa ba, in ji madam Tax a cikin wata hirarta tare da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua a yayin dandalin shugabannin kasashe da gwamnatocin kungiyar SADC karo na 34. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China