in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kashe ma'aikatan jin kai biyu 'yan kasar Mali a arewacin kasar
2014-05-31 16:14:57 cri
Wasu ma'aikatan jin kai 'yan kasar Mali na wata kungiyar kasar Norvege dake kula da 'yan gudun hijira (NRC) sun hallaka a ranar Alhamis bayan motar dake dauke da su ta taka nakiya a kan hanyar Goundam zuwa Tombouctou a arewacin kasar Mali in ji wata majiya mai tushe.

A cewar kungiyar NRC, wata kungiya mai zaman kanta dake aiki tare da kungiyar kula da 'yan gudun hijira ta MDD, ma'aikatan biyu sun dawo da kammala aikinsu na rarraba wasu kayyakin bukatun yau da kullum ga 'yan gudun hijira da suka shiga baya bayan nan cikin wannan yanki.

A cikin wannan sanarwa, babban jami'in dake kula da ayyukan jin kai a kasar Mali, David Gressly yayi allawadai da wadanda suka haddasa mutuwar wadannan ma'aikatan biyu.

Akwai bacin rai matuka, ma'aikatan jin kai su mutu a yayin da suke kokarin kai taimako ga mutanen dake cikin mawuyacin hali. Ina kira ga dukkan bangarorin da wannan rikicin kasar Mali ya shafa dake arewacin kasar dasu kiyaye tsaron lafiyar fararen hula da kuma bada dama ga kungiyoyin agaji don su kai taimako ga mutane in ji mista Gressly.

A cewar wannan sanarwa, kusan kungiyoyin bada agaji dari ne na kasar Mali dana kasashen waje suke wannan kasa dake yammacin Afrika inda suke kai taimakon ruwan sha, abinci, bada jinya da matsugunni ga miliyoyin mutanen kasar Mali. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China