in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tarayyar Turai EU ta yi maraba da kaddamar shawarwari na tsakanin 'yan kasar Mali
2014-07-19 16:26:31 cri
Kungiyar tarayyar Turai EU ta bayyana gamsuwarta a ranar Jumma'a kan kaddamar da shawarwari na tsakanin 'yan kasar Mali a ranar Laraban da ta gabata a birnin Alger na kasar Aljeriya.

Kakakin ma'aikatar kungiyar tarayyar Turai game da harkokin waje (SEAE) ya yi maraba da matsayin Aljeriya a wannan fanni, tare da taimakon kungiyar ECOWAS, tarayyar Afrika AU, MDD, EU da kuma kungiyar kasashen musulmi ta OCI, tare da taimakon kasar Burkina Faso, Mauritaniya, Nijar da Chadi dake halartar wadannan shawarwari na manyan jami'ai.

Haka kuma kakakin ya jaddada goyon bayan kungiyar Turai da ci gaban wannan zaman tebur, domin cimma hanyoyi masu nagarta na aiwatar da niyyar dukkan bangorin da abin ya shafa ga taimakawa zaman lafiya da sansanta 'yan kasar Mali ciikin karko. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China