in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Mali ta cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta tare da 'yan yawaye
2014-05-24 17:03:11 cri
Gwamnatin kasar Mali ta cimma wata yarjejeniyar tsagaita bude wuta a ranar Jumma'a tare da manyan kungiyoyin 'yan tawaye guda uku dake arewacin kasar Mali, tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD domin kawo karshen rikicin da kasar take fama da shi ce ta fitar da wannan labari.

Kungiyar MNLA, kwamitin hadin kan yakin Azawad na HCUC da kuma 'yan tawayen Larabawa na yankin Azawad (MAA) sun cimma rattaba hannu a kanta a daren jiya, in ji tawagar MDD dake kasar.

Wannan sanarwa ta biyo bayan tattaunawar shiga tsakani a karkashin jagorancin shugaban kasar Mauritaniya Mohamed Ould Abdel Aziz dake kuma shugaban tarayyar Afrika a wannan karo.

Sake barkewar rikici na baya bayan nan a arewacin kasar Mali ya janyo kara barazanar kara tura wannan kasa dake yammacin Afrika cikin tashin hankali da zaman dar dar wanda kuma ba ta jima da samun zaman lafiya ba. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China