in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya taya kasar Mali murnar cimma yarjejeniyar sulhuntawa a tsakanin bangarorin kasar daban-daban
2014-07-25 15:46:39 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya bayar da wata sanarwa ta hannun kakakinsa a daren ranar 24 ga wata, inda ya taya kasar Mali murnar cimma yarjejeniyar sulhuntawa tsakanin bangaroiri daban-daban da ke kasar, kana ya yi kira ga bangarori daban daban na kasar da su dakatar da yake-yake da juna ba tare da bata lokaci ba.

Sanarwar ta bayyana cewa, Ban Ki-moon ya nuna damuwa sosai kan hali mai tsanani da ake ciki a wasu yankuna dake arewacin kasar Mali, ciki har da rikice-rikicen da dakaru suka tada.

Ban Ki-moon ya nuna cewa, wadannan rikice-rikice sun saba wa yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma a Ouagadougo a watan Yuni na shekarar 2013 da kuma irinta da aka daddale a ranar 23 ga watan Mayu na bana.

Don haka ya yi kira ga bangarori daban daban da abin ya shafa da su dakatar da yake-yake da juna, kana su yi hadin gwiwa da hadadden kwamitin tsaro da ke karkashin jagorancin tawagar kiyaye zaman lafiya ta MDD da ke Mali. A cewar Ban ki-Moon, wannan matakin zai taka muhimmiyar rawa ga tattaunawar neman samun sulhuntawa da ake yi a tsakanin bangarori daban daban na kasar Mali,

A ranar 16 ga wata ne, gwamnatin kasar Mali da dakaru masu adawa suka fara yin shawarwari a tsakaninsu a birnin Algeis, babban birnin kasar Algeria, inda suka sanya hannun kan yarjejeniyar sulhu a tsakanin sassa daban-daban na kasar a ranar 24 ga wata. Hakan ana sa ran ganin kawo karshen tashe-tashen hankali da ake fama da su a arewacin kasar. Saidai bangarorin biyu za su kaddamar da wani sabon shawarwari a tsakiyar watan Agusta na bana. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China