in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin raya Afirka zai bada rancen kudi dala biliyan daya ga kasar Angola
2014-07-29 14:44:11 cri
Ministan kudi na kasar Angola Armando Manuel, ya ce gwamnatin kasar Angola ta daddale wata yarjejeniya da bankin raya Afirka, wadda za ta baiwa kasar damar samun rancen kudi dala biliyan daya. Kudaden da ake fatan za su taimakawa kasar, wajen gudanar da kasafin kudinta yadda ya kamata.

Mr. Manuel ya bayyana hakan ne bayan da shugaban kasar Angola Jose Eduardo dos Santos, ya gana da shugaban bankin raya Afirka Donald Kaberuka a jiya Litinin.

Kaza lika Manuel ya kara da cewa, ana sa ran bankin na raya Afirka, zai samar da dala miliyan 600 a matsayin kashin farko na wannan rance a cikin watan Agusta mai zuwa, wanda kuma kasar ta Angola za ta yi amfani da shi a fannonin ginin ababen more rayuwa, da sufuri da kuma samar da makamashi.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, kamfanonin kasashen waje da dama sun nuna rashin jin dadi, na rashin damar samun dalar Amurka a bankunan kasar ta Angola, don haka ake fatan wannan rance da bankin na raya Afirka zai baiwa kasar Angola, zai sassauta wannan matsalar ta rashin samun kudaden kasashen waje da bankunan kasar ke fuskanta. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China