in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Angola ta yaba wa gudummawar da masana'antun Sin da suka ba da ga sha'anin wasannin motsa jiki na kasar
2014-02-18 16:13:21 cri
Kwanan baya, a gun bikin kaddamar da kulab na wasannin motsa jiki na Kilamba Kiaxi wato K.K., ministan dake kula da harkokin wasannin motsa jiki na kasar Manuel Muandumba ya yaba wa gudummawar da kamfanin CITIC na kasar Sin ya bayar ga sha'anin wasannin motsa jiki na kasar, musamman ma ya jinjinawa kamfanin bisa ga goyon bayan da yake nunawa wajen raya wasan kwallon tebur tsakanin matasan kasar, lamarin da ya sa matasan kasar suka samu babban ci gaba a wannan fanni.

Kulab na wasannin wato kulab K.K. tana yankin kudancin birnin Luanda na hedkwatar kasar, kuma fadin filin kulab din ya kai murabba'in mita dubu 130.Kamfanin CITIC na kasar Sin ba ma kawai ya fasalta wannan kulab, har ma ya gina filayen wasan kwallon kafa guda 2 da fadinsu ya kai murabba'in mita dubu 15.

Bayan da kamfanin CITIC ya fara aiki a kasar Angola cikin shekaru sama da 5 da suka gabata, ya samar da guraben ayyukan yi sama da dubu 10 a wurin, inda suka bude makarantun horas da ma'aikatan gine-gine, da horar da ma'aikata ba tare da biyan ko sisi ba, kuma ya tashi tsaye don gina hanyoyin dogo, da gidaje, da haka rijiyoyi, da gina makarantu a kyautu. Haka kuma, wannan kamfani ya ba da kudi don raya wasannin kwallon tebur, da kwallon raga, da wasan dambe da sauransu, abun da ya sa Angola ta cimma burin samun lambobin yabo a wasannin kwallon tebur na cin kwafin Afrika.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China