in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Angola ta jaddada muhimmancin rawar da MDD ke takawa wajen wanzar da zaman lafiya da ci gaba
2013-09-28 17:02:58 cri
Mataimakin shugaban kasar Angola Manuel Domingos Vicente, ya jaddada muhimmancin irin rawar da MDD ke takawa a fagen wanzar da zaman lafiya da samar da ci gaban rayuwar bil'adama.

Vicente wanda ya bayyana hakan ranar Jumma'a 27 ga wata, yayin da yake tsokaci gaban mahalarta babban taron MDD na shekara-shekara da ke gudana a hedkwatar Majalissar dake birnin New York, ya ce kasarsa na matukar imani da tasirin da MDD ke da shi, wajen tabbatar da yanayin zaman lafiya, da daidaito, tare da kwarewar samar da kandagarkin barkewar tashe-tashen hankula a dukkanin sassan wannan duniya.

A cewarsa taron na bana na zuwa ne a gabar da ake matukar bukatarsa, duba da irin halin rigingimu da dake addabar sassan duniya daban-daban.

Daga nan sai mataimakin shugaban kasar ta Angola ya nanata bukatar daukar dukkanin matakan da suka wajaba, wajen magance dimbin matsalolin dake addabar al'umma, ciki hadda batun yaduwar kananan makamai, da ayyukan ta'addanci, da fashin teku, da cinikayyar muggan kwayoyi, da kuma kangin talauci dake addabar al'ummun dake sassan duniya da dama. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China