in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An cafke wanda ake zargi da dasa bom a makarantar koyon aikin kiwon lafiya ta Kano
2014-06-24 10:40:55 cri
'Yan sanda a tarayyar Najeriya sun tabbatar da cafke wasu mutane da ake zargi da dasa bom a makarantar koyon aikin kiwon lafiya dake birnin Kano a arewacin kasar.

Babban jami'in hukumar 'yan sandan jihar Kano ya bayyana wa 'yan jarida a wurin da bam din ya tashi cewa, an riga an damke wanda ake zargi da dasa shi, kuma a yanzu haka ana ci gaba da bincike kan lamarin kafin gabatar da karin bayani ga kafofin watsa labaru.

Bisa bayanan da mahukuntan kasar suka bayar, an ce ya zuwa yanzu, yawan mutanen da suka mutu a sakamakon lamarin ya kai 8. Koda yake wasu shaidu da suka ganewa idanun su aukuwar lamarin sun ce, yawan wadanda suka rasu ya kai akalla mutum 18.

Ya zuwa yanzu dai, babu wata kungiya ko wani mutum da ya dauki alhakin kai wannan hari, koda yake dai bangarori daban daban a kasar na zargin kungiyar Boko Haram wadda a baya ta sha kaddamar da makamantan wadannan hare-hare. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China