in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Nijeriya sun murkushe wani gungun hukumar leken asiri ta Boko Haram
2014-07-01 10:27:03 cri
Sojojin tarayyar Nijeriya sun sanar da murkushe gungun leken asirin Boko Haram a ranar 30 ga watan Yuni, wanda yake da hannu a ayyukan garkuwa da dalibai mata na makarantar sakandare fiye da dari biyu a watan Afrilu na bana.

Kakakin ma'aikatar tsaron kasa ta tarayyar Nijeriya Chris Olukolade wanda ya bayar da wata sanarwa a wannan rana, ya ce, wani mutum mai suna Babuji Ya'ari ya jagoranci wannan gungun, wanda shi dan kasuwa ne mai sayar da motocin keke Napep wato mai tayoyi 3, kana shi memban kungiyar 'yan banga ne dake wurin. Ya'ari ya yi amfani da matsayinsa don gudanar da ayyukan leken asiri.

Janar Olukolade ya kara da cewa, tun daga shekarar 2011 zuwa yanzu, Ya'ari ya bada gudummawa wajen kai hare-hare a garin Maiduguri na jihar Borno dake arewa maso gabashin tarayyar Nijeriya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China