in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Isra'ila ta ci gaba da kai hare-hare ta sama a Gaza
2014-07-11 10:21:51 cri
A jiya Alhamis 10 ga wata ne aka shiga yini na uku tun bayan da sojojin Isra'ila suka fara kaddamar da hare-hare kan yankunan al'ummar Falasdinawa, bisa abin da suka kira kiyaye tsaron iyakar kasar Isra'ila, wanda ya zuwa yanzu ya haddasa mutuwar Falasdinawa 86, yayin da sama da 500 suka jikkata.

Ma'aikatar kiwon lafiya ta Falesdinu ta sanar da cewa, galibin mutanen da suka rasu fararen hula ne ciki har da mata da yara da dama.

A jawabin da firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu ya yi yayin taron kwamitin kula da harkokin diplomasiyya da tsaron kasa da ke majalisar dokokin kasar ta Isra'ila, da aka gudanar a ran 10 ga wata, ya ce, a halin yanzu, kasar ba ta da wani shirin kulla yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kungiyar Hamas.

A wannan rana kuma, shugaban Felesdinu Mahmoud Abbas ya yi shawarwari da ministan harkokin wajen kasar Amurka John Kerry ta wayar tarho, inda ya yi fatan cewa, bangarorin biyu za su yi kokari tare, domin tsagaita bude wuta a yankin Gaza cikin hanzari.

A wani ci gaban kuma, shi ma shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya yi shawarwari tare da firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu ta wayar tarho, inda ya jaddada cewa, tilas ne kasar Isra'ila ta dakatar da hare-haren da ta kai ba tare da bata lokaci ba.

Bugu da kari, shugaban kasar Faransa Francois Hollande ya yi kira ga Isra'ila da Falesdinu da su kai zuciya nesa, kana su fara yin shawarwari a tsakaninsu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China