in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Li Keqiang ya gana da shugabar gwamnatin Jamus Merkel
2014-07-07 10:05:32 cri

Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya gana da shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel a nan birnin Beijing a ranar 6 ga wata.

A yayin ganawar, Li Keqiang ya nuna cewa, kasar Sin ta maida aikin samun ci gaba a matsayin aikin dake gaban kome, da kuma yin kokarin kyautata rayuwar jama'a da farko, sai dai ana bukatar yanayi na zaman lafiya a duniya yayin da ake kokarin samun bunkasuwa. Kana kasar Sin za ta ci gaba da bin hanyar samun bunkasuwa cikin lumana, kuma tana son yin kokari tare da kasa da kasa ciki har da Jamus wajen kirkiro wata duniya mai zaman lafiya da wadata har abada.

A nata bangare, Merkel ta bayyana cewa, kasar Jamus tana son kara yin hadin gwiwa a tsakaninta da kasar Sin, da kiyaye mu'amala tare da Sin kan harkokin kasa da kasa da yankuna, da sa kaimi da a inganta dangantakar kasashen biyu da kiyaye zaman lafiya da bunkasuwa tare. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China