in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani manzon musamman na Ban Ki-moon ya kai goyon bayan MDD ga kasar Guinee
2014-04-19 16:10:55 cri
Tun bayan barkewar cutar dake haddasa zubar da jini ta Ebola yau da kusan watannin uku dake cigaba da kawo ta'adi a kasar Guinee, mataimakin sakatare janar na MDD dake kula da harkokin siyasa Jeffrey Feltman ya samu ganawa a ranar Jumma'a a birnin Conakry tare da shugaban kasar Guinee Alpha Conde.

A yayin tattaunawar, jami'an biyu sun maida hankali kan matsalar cutar Ebola ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 122 tare da fiye de mutane 190 dake fama da cutar wadanda ke samun jinya a cibiyoyin dake yankunan da annobar ta fi shafa.

Manzon musamman na MDD ya bayyana damuwar MDD kan wannan annoba data shafi kasashe da dama na yammacin Afrika, inda Guinee ta fi samun yawan mutanen da suka mutu a matsayin kasar wannan cuta ta barke.

A matsayin ziyarar gani da ido a yammacin Afrika, akwai muhimmanci waje na in kawo ziyara Guinee dake huldar dangantaka mai karfi tare da MDD in ji mista Feltman kafin ya kara da cewa ziyararsa tana nuna goyon baya ga gwamnati da jama'ar Guinee.

Haka kuma da sunan babban sakatare janar na MDD, mista Feltman ya nuna cewa ziyararsa ta kasance wata dama domin tattaunawa tare shugaban Guinee kan batutuwan siyasa, musamman kan girmama yarjejeniyoyin siyasar fita daga rikici da aka rattaba wa hannu a cikin watan Yulin shekarar 2013 tsakanin bangarorin siyasar kasar Guinee da kuma kafa sabuwar majalisar dokoki. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China