in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An samu sabbin masu dauke da cutar ebola su 42 a yammacin Afrika
2014-04-18 20:37:59 cri
Hukumar kiwon lafiya ta MDD ta sanar da cewa rahotannin na nuna samun Karuwar mutanen dake dauke da cutar ebola har su 42 a yammacin nahiyar Afrika a cikin kwanaki ukku.

A shafin yanar gizon hukumar da aka buga a ranar alhamis din nan an ce wadanda suka mutu sakamakon cutar sun karu daga 121 zuwa 137 a cikin kwanaki ukku, inda yawancin wadanda suka mutu a kwanakin baya, ko kuma kashi 87% daga cikinsu, 'yan kasar Guinea ne.

Adadin wadanda ake zargi da wadanda aka tabbatar da kamuwa da cutar a Guinea,da Liberiya da kuma Saliyo sun haura daga 194 zuwa 236 a cikin kwanaki ukku da suka wuce. Wanda yawancin sabbin masu dauke da cutar sun fito ne daga kasashen Guinean da kuma Saliyo. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China