in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban hukumar FIFA ya yi Allah wadai da fashewar bom da ta faru a wani wurin kallon kwallo a Nijeriya
2014-06-19 14:24:06 cri
Shugaban hukumar wasan kwallon kafa ta duniya wato FIFA Joseph S. Blatter ya yi Allah da fashewar bom a wani gidan kallon kwallo dake birnin Damaturu a arewacin kasar Nijeriya a ranar 17 ga wata da dare.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, ya zuwa yanzu, yawan mutane da suka mutu a sakamakon fashewar bom din ya kai 14, kana mutane 26 sun ji rauni.

Fashewar bom din ta faru a ranar 17 ga wata da misalin karfe 8 da minti 15 da dare, yayin da jama'a suke kallon gasar cin kofin duniya a tsakanin Brazil da Mexico. Wani mutum da lamarin ya faru gabansa ya bayyana cewa, an dana bom din a kan wani babur mai tayoyi 3, karfin tashin bom din ya lalata gine-ginen dake dab da wurin.

A nasu bangare 'yan wasan kungiyar kasar Nijeriya dake halartar gasar cin kofin duniya a kasar Brazil sun yi allah wadai da lamarin. Emmanuel Attah, wani jami'in kungiyar ya bayyana cewa, 'yan wasan za su kara yin hadin kai da kokarin samun sakamako mai kyau don jajantawa masu sha'awar wasan a cikin gida. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China