in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron koli na kungiyar AU karo na 23
2014-06-27 14:57:39 cri
An bude taron koli na kungiyar AU karo na 23 mai taken "bunkasa noma da tsaron hatsi" a birnin Malabo na kasar Equatorial Guinea a ranar 26 ga wata, wanda za a shafe kwanaki biyu ana yinsa, inda shugabanni da kusoshin kasashe membobin kungiyar AU fiye da 50 za su yi shawarwari kan batutuwan bunkasa aikin gona, tabbatar da tsaron hatsi, kiyaye zaman lafiya da gabatar da burinsu na nan gaba da dai sauransu.

Shugabar kwamitin kungiyar AU Nkosazana Dlamini-Zuma ta yi wani jawabi a gun bikin kaddamarwar taron, inda ta yi kira ga kasashen Afirka da su kafa tsarin aikin gona na zamani, kirkiro sabbin fasahohin aikin gona da kuma inganta sha'anin sarrafa amfanin gona.

A gun taron, babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya bayyana cewa, ana samun zaman lafiya da bunkasuwar tattalin arziki a yawancin kasashen Afirka, kuma an samu ci gaba yayin da ake yin kokarin cimma burin muradun karni na MDD. Kana yayin da ake kokarin cimma burin shekarar 2063 a Afirka, MDD tana son yin hadin gwiwa tare da kungiyar AU don sa kaimi ga samun zaman lafiya da bunkasuwa mai dorewa a Afirka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China