in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya yi Allah wadai da sacen 'yan mata a Najeriya
2014-05-10 17:11:29 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya fitar da wata sanarwa a ran 9 ga wata, inda ya yi suka kan hare-hare da sacen 'yan mata a kasar Najeriya kwanan baya, tare da yin kira da a saki wadannan 'yan mata cikin gaggawa.

Sanarwar ta bayyana cewa, kungiyar Boko Haram ta kai hare-hare a birnin Gamboru Ngala dake jihar Bornon Najeriya a ran 5 ga wata, lamarin ya haddasa mutuwa da jakkata mutane da dama. Kwamitin sulhu na MDD na kuma Allah wadai da hare-haren Boko Haram, a sa'i daya kuma, kwamitin ya nuna juyayinsa ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu cikin hare-haren kungiyar Boko Haram, da kuma jama'a da gwamnatin kasar, tare da fatan samun sauki ga wadanda suka jikkata.

Kwamitin sulhu na MDD ya ce zai ci gaba da mai da hankali kan halin da 'yan matan da aka sace suke ciki, da kuma batun daukar matakai kan kungiyar Boko Haram. Haka zalika, kwamitin ya jadadda cewa, duk wani ta'addanci ya kasance babbar barazana ga zaman lafiya da tsaron kasa da kasa, kuma babban laifin da ya kamata a hukunta. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China