in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kwace hauren giwaye 228 a kasar Kenya
2014-06-06 10:39:30 cri
Hukumar kula da namun daji ta kasar Kenya, ta bayyana cewa, 'yan sandan kasar sun kwace hauren giwaye 228 da wasu sassan na hauren giwaye 74, da ke boye a birnin Mombasa.

Wani jami'in hukumar Arthur Tuda ya bayyanawa manema labaru cewa, bisa binciken da aka yi kan launi da girman wadannan hauren giwaye, an gano cewa na giwaye ne irin na kasar Kongo Kinshasa, da Tanzaniya, da wurin yawon shakatawar Tsayo dake kasar Kenya da dai sauransu.

Mr. Tuda ya ce, an kasha giwayen da yawan su ya haura dari daya kafin tattara hauren giwaye mai wannan yawa.

Shi ma a nasa bangare babban jami'in rundunar 'yan sandan birnin Mombasa Geoffrey Mayek, cewa ya yi jami'an sa suna bincike kan wani mutum 'dan asalin kasar Kenya, da ake zargi da laifin fasa-kwaurin hauren giwayen, kana ana neman sauran mutanen da suka taimaka wajen aikata wannan laifin.

Rundunar 'yan sandan dai na zargin 'yan ta'adda, da tattara kudade ta hanyar fasa-kwaurin hauren giwaye a yankunan dake dab da tekun kasar ta Kenya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China