in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Fashewar wasu abubuwa a Nairobi ya haddasa mutuwar mutane a kalla 10
2014-05-17 17:11:56 cri
'Yan sandan kasar Kenya sun sanar a Jumma'a 16 ga wata da cewa, an ji fashewar jerin wasu abubuwa guda 2, wadanda ake tsammanin nakiyoyi ne, a Nairobi, babban birnin kasar lamarin da ya yi sanadiyyar rasa rayukan mutane a kalla 10, kana 70 kuma suka jikkata.

Wani babban jami'i mai kula da 'yan sandan birnin Nairobi ya gaya ma manema labaru cewa, fashewar ababen guda 2 sun abku ne a wani yankin dake dab da babbar kasuwar Gikomba. A cewarsa tashin abun na farko ya faru a cikin wani karamin bas dake daukar fasinjoji 14, yayin da fashewa ta biyu ta faru a cikin kasuwar Gikomba. Jami'in ya kara da cewa ba a san dalilin fashewar ababen ba tukuna, amma 'yan sanda sun riga sun cafke mutum daya wanda ake tuhumarsa da hannu a cikin wannan lamarin.

Kasuwar Gikomba da aka samu fashewar ababen ita ce daya daga cikin manyan kasuwannin birnin Nairobi, kana an ta da wadannan abubuwa 2 ne a lokacin da ake samun cunkuson jama'a cikin kasuwar. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China