in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin ladabtarwa na kasar Sin zai kara daukar matakai wajen farautar masu cin hanci da suka gudu zuwa kasashen waje
2014-05-30 15:14:05 cri
A ranar 29 ga wata, kwamitin ladabtarwa na kasar Sin ya gudanar da taron tattaunawa kan farautar masu cin hanci da suka gudu zuwa kasashen waje, inda ya ce, za a kara daukar matakai wajen kama masu cin hanci dake kasashen waje, da kuma yanke musu hukunci.

A gun taron, mataimakin sakataren kwamitin ladabtarwa da ya shugabancin taron Huang Shuxian ya jaddada cewa, kama masu cin hanci da kuma kwato kudaden da suka sata muhimman ayyuka ne wajen yaki da cin hanci, kana wata mihimmiyar hanya ce wajen hana yaduwar matsalar cin hanci da rashawa.

Hakazalika Mr Huang ya nuna cewa, aikin kama masu cin hanci a kasashen waje da kuma kwato kudaden da suka sata wani aiki ne mai sarkakkiya, wanda ke bukatar hadin gwiwa a fannonin diplomasiyya, dokoki, da hada-hadar kudi. Kamata ya yi hukumomin da abin ya shafa su bada fifikonsu, da hadin kansu don ba da gudummowa ga wannan aikin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China