in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kama jami'ai fiye da 36900 da ake tuhumarsu da laifin cin hanci da karbar rashawa daga watan Janairu zuwa Nuwamban bara a kasar Sin
2014-01-05 16:38:56 cri
An samu labari daga babbar hukumar gabatar da kararraki ta kasar Sin cewa, hukumomin gabatar da kararraki na kasar Sin sun aiwatar da ayyukan da kwamitin tsakiya na jam'iyyar JKS ya dora musu a tsanake, inda suka kara karfin yaki da cin hanci da karbar rashawa. An ce, daga watan Janairu zuwa Nuwamba na shekarar 2013 da ta gabata, hukumomin sun bi bahasin laifuffukan cin hanci da karbar rashawa guda 27236 tare da kama wadanda ake tuhumarsu da laifuffukan 36907

A yayin da hukumomin gabatar da kararraki na kasar Sin suke kokarin bin bahasin manyan laifuffuka, sun mai da hankali sosai kan laifuffukan cin hanci da karbar rashawa, wadanda suka abku a cikin ma'aikatun gwamnatin kasar. Tun daga watan Janairu zuwa Nuwamban bara, an bi bahasin irin wadannan laifuffuka guda 16510 tare da kama mutane 23017, wadanda suka lalata dukiyar kasa. Yawan kudaden da wadannan laifuffuka suka shafa ya zarce kudin Sin RMB yuan biliyan 5 da miliyan 510.

Yayin da hukumomin gabatar da kararraki na kasar Sin a matakai daban daban suke rubanya kokarinsu na bin bahasin manyan laifuffuka, su ma sun zurfafa bincike kan laifuffukan da suka shafi muhimman fannonin raya tattalin arziki da zaman al'ummar kasa, da kuma lalata moriyar jama'ar kasar, sa'an nan sun yi ta kara karfinsu na kama wadanda ake tuhumarsu da laifuffukan, da kuma maido da kudaden da aka sata, sun yanke hukunci mai tsanani kan mutanen da suka aikata mabambantan laifuffukan cin hanci da karbar rashawa bisa doka yadda ya kamata. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China