A nasa jawabin, gwamnan jihar Kogi Idris Wada ya ce, kamfanin Kaibo na kasar Sin ya shigo Najeriya ne a shekara ta 2012. A kuma cikin shekaru biyu da suka wuce, kamfanin ya samu ci gaba sosai a Najeriya. Yayi imanin cewa, kamfanin Kaibo zai kammala aikin gina babban ginin na jihar Kogi a kan lokaci kuma yadda ya kamata.