Mataimakin shugaban Najeriya Namadi Sambo ya ce, babban ginin jihar Kogi da kamfanin kasar Sin zai fara, zai zamo gini mai jawo hankalin mutane a Abuja, saboda sabon salon da yake tattare da shi. Sambo ya kuma yaba da matukar kokari, da gudummawar da kamfanin Kaibo ke bayarwa a fannonin raya tattali arziki, da samar da guraben ayyukan yi, da kuma kyautata zaman rayuwar al'umma a Najeriya.