in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'o'in kasar Sin 18 za su karbi dalibai daga Afirka ta Kudu
2014-05-19 14:48:54 cri

Za a shirya bikin nune-nunen ba da ilmi na kasar Afirka ta Kudu daga ranar 19 zuwa 21 ga wata. A ranar Lahadi 18 ga wata, wakilan jami'o'in kasar Sin sun shirya wani taro a birnin Johannesburg, don gabatar da nune-nunensu tare kuma da zantawa da manema labaru.

Bisa shirin da hukumar ba da tallafin karo ilimi ta ma'aikatar ba da ilmi ta kasar Sin ta tsara, bikin nune-nunen zai samu halartar shugabanni da ma'aikatan jami'o'i 18 na kasar Sin, inda za su karbi dalibai daga kasar Afirka ta Kudu.

Wadannan jami'o'i suna fatan kafa hukumomin karbar dalibai a Afirka ta Kudu, inda za su iya kara karbar nagartattun dalilai daga kasar, a sa'i daga kuma za su iya samar da dama ga yaran Sinawa da ke zama a Afirka ta Kudu wajen dawowa kasar Sin don kara ilmi. (Danladi)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China