in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
ANC ce kadai zabin akasarin 'yan Afirka ta Kudu inji shugaba Zuma
2014-05-11 15:58:02 cri
Shugaba Jacob Zuma na Afirka ta Kudu ya ce jam'iyyar sa ta ANC ce zabi na hakika ga mafi yawan al'ummar kasar, musamman ma talakawa da ma'aikata.

Shugaba Zuma ya bayyana hakan ne jiya Asabar, bayan bayyana sakamakon babban zaben kasar na bana, zaben da ANC mai mulkin kasar ta lashe da gagarumin rinjaye.

Cikin jawabin da ya gabatarwa al'ummar Afirka ta Kudun, Mr. Zuma ya ce ANC za ta yi amfani da rinjayen ta, wajen aiwatar da manufofin da za su bunkasa rayuwar jama'a a dukkanin fannonin ci gaba.

Ya ce gwamnatin sa za ta ci gaba da daukar matakan samarwa al'ummar kasar ababen more rayuwa, da suka kunshi tsaftataccen ruwan sha, da hanyoyi, da lantarki, da inganta kiwon lafiya da ilimi da dai sauran su.

Sakamakon karshe da hukumar gudanar da zaben kasar mai zaman kanta IEC ta fitar dai ya nuna cewa, ANCn ce ke gaba da kaso 62.15 na daukacin kuri'un da aka kada, yayin da babbar jam'iyyar adawa ta DA ke matsayi na biyu da kaso 22.23 bisa dari na jimillar kuri'un. (Saminu Alhassan Usman)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China