in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bayyana sakamakon babban zaben kasar Afirka ta Kudu
2014-05-10 17:21:43 cri
Bisa sabon sakamakon zaben majalisar dokokin kasar Afirka ta Kudu da kwamitin zabe mai zaman kansa ya gabatar, an ce, jam'iyyar ANC mai mulkin kasa ta lashe zaben tare da yawan kuri'u sama da kashi 60 bisa dari, yayin da babbar jam'iyyar adawa ta samu kuri'u kashi 22 bisa dari.

Wannan shi ne karo na biyar da ake gudanar da zaben majalisar dokokin kasar Afirka ta Kudu, tun bayan kawo karshen wariyar launin fata a shekarar 1994. Bugu da kari, wannan shi ne karo na farko da aka gudanar da zaben majalisar dokokin kasar tun bayan rasuwar tsohon shugaban kasar Nelson Mandela.

Bisa tsarin mulkin kasar Afirka ta Kudu, idan 'yan kasar Afrika ta Kudu suka zabi sabuwar majalisar dokokin kasa da farko, sa'an nan kuma, majalisar dokokin kasa ta zabi shugaban kasa a birnin Cape Town a ran 21 ga wata, a karshe a gudanar da bikin rantsar da shugaba da ministocin kasar a birnin Pretoria a ran 24 ga wata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China