in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha na zargin Ukraine da sabawa yarjejeniyar Geneva
2014-05-16 10:59:46 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha Alexander Lukashevich ya bayyana a ran 15 ga wata cewa, matakan da gwamantin kasar Ukraine ta dauka kwanan baya ya saba wa yarjejeniyar Geneva kan batun Ukraine da kasashe hudu da batun ya shafa suka cimma, wadanda suka kunshe da Ukraine din kanta, Kungiyar EU, Amurka da kuma Rasha.

A yayin taron manema labaran da aka yi a wannan rana, Mr. Lukashevich ya bayyana cewa, kasarsa ta damu matuka kan yadda al'amura ke tabarbarewa a kasar ta Ukraine, kuma gwamantin kasar Ukraine na ci gaba da keta hakkin jama'arta.

A wannan rana kuma, ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha ta ba da wata sanarwar, inda ta nuna cewa, ya kamata a fara gudanar da taron sulhunta al'ummar Ukraine, a kokarin da ake na yin kwaskwarima ga tsarin mulkin kasar, ta yadda za a iya tabbatar da shigar da dukkan bangarorin siyasa dake sassa daban daban na kasar cikin wannan yunkuri.

A nata bangare kuma, ma'aikatar harkokin wajen kasar Ukraine ta ba da wata sanarwa, inda ta nuna rashin jin dadinta kan atisayen soja da kasar Rasha ta yi a kan iyakar kasashen biyu, inda ta bukaci kasar Rasha da ta janye sojojinta daga wannan yanki. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China