in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'an tsaro sun gano makamai a jihohin Benue, Plateau da Kaduna dake Najeriya
2014-05-08 20:57:53 cri

Jami'an tsaron Najeriya dake gudanar da ayyukan bincike a yankunan arewa ta tsakiya, da yammacin kasar sun gano wasu makamai a wadannan yankuna.

A yayin wani binciken da suka gudanar a garin kira Anyibe dake karamar hukumar Logo ta jihar Benue, jami'an tsaron sun gano wasu makamai mallakar wani matashi, wanda ke cikin gungun masu tada zaune-tsaye a yankin. Jami'an tsaro sun gano bindigogi biyar, da wasu sauran makamai masu hadari. Yanzu haka dai ana tsare da wannan matashi domin ci gaba da bincike.

Haka kuma a jihar Plateau, jami'an tsaro sun gano bindigogi guda biyar da sauran wasu makamai, a wata mafakar 'yan ta da zaune-tsaye dake yankunan Hukke da Reweinko.

Labarai daga jihar Kaduna, wadda ke arewacin Najeriya ya shaida cewa, a yayin wani artabu da jami'an tsaro suka yi da 'yan ta da-kayar-baya a garin Kwandaga, mutane da dama sun samu raunuka, kuma an gano makamai da yawa.

Darektan yada labarai na hukumar tsaron kasar manjo-janar Chris Olukolade, wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar jiya a Abuja, ya ce binciken da ake gudanarwa a yankin yana daga cikin kokarin da hukumarsa ke yi, don ganin an samar da zaman lafiya a yankunan da ma kasa baki daya.

Murtala, wakilin sashin Hausa na CRI, daga Abuja, Najeriya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China