in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kocin Najeriya ya fidda sunayen 'yan wasansa na wucin gadi
2014-05-08 20:53:58 cri
Babban mai horas da 'yan wasan kwallon kafar Najeriya Stephen Keshi, ya fidda sunayen 'yan wasa 30, wadanda daga cikin su za a zabi 23 da za su bugawa Super Eagles wasanni, a gasar cin kofin duniya dake tafe a kasar Brazil.

Rahotanni sun bayyana cewa Keshi ya fidda jerin sunayen ne a ranar Talata a birnin Abuja fadar mulkin Najeriya, bayan kammala zaman kwamitin tsare-tsare na hukumar kwallon kafar kasar. Ya ce 'yan wasan da aka zayyana za su bugawa kulaf din wasannin sada zumunci da kasashen Greece da Amurka da Scotland. Za kuma a sanar da sunayen 'yan wasa 23, da za a yi gasar cin kofin na duniya da su a ranar 2 ga watan Yunin dake tafe.

Yanzu haka dai ana sa ran 'yan wasan da aka gayyata za su isa sansanin kungiyar dake kasar Birtaniya, a ranar 25 ga watan nan na Mayu, domin shirin fuskantar takwarorin su na Scotland a wasan sada zumunci da tuni aka shirya bugawa ran 28 ga watan nan. Sai kuma wasannin sada zumuncin da Super Eagle din za ta yi da Greece ran 3 ga watan Yuni, yayin da wasan ta da Amurka zai kasance ran 7 ga watan na Yuni.

Sunayen 'yan wasan da aka fitar dai ya nuna cewa ba a gayyaci mai tsaron baya kungiyar Ike Uche ba, wanda aka maye gurbinsa da Leon Balogun, dake bugawa kulaf din Fortuna Dusseldorf na kasar Jamus kwallo. Shi ma a dan gaban kungiyar Bright Dike, wanda ya ci wa Super Eagles din kwallo a wasan sada zumunci da aka tashi 1 da 1 da Catalonia bai samu gayyatar ba.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China