in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Karfin cinikayyar dake tsakanin Sin da Afirka ya kai sama da dallar Amurka biliyan dari 2 a shekarar 2013
2014-04-22 20:43:06 cri
Dangantakar tattalin arziki da cinikayya dake tsakanin kasar Sin da nahiyar Afirka na ci gaba da bunkasa cikin yanayi mai kyau, abin da ya kai wani sabon matsayi a shekarar 2013. Karfin cinikayyar dake tsakanin bangarorin biyu ya kai dallar Amurka biliyan 210.2, adadin da ya karu da kashi 5.9 bisa dari idan aka kwatanta da na shekarar 2012.

Bayanin haka ya fito ne sakamakon wani taron dandalin kara wa juna sani game da harkokin zuba jari da sha'anin kudi a tsakanin kasar Sin da nahiyar Afirka na shekarar 2014, da kungiyar kasuwancin kasa da kasa ta kasar Sin da bankin Chartered suka gudanar tare a nan birnin Beijing.

A shekarar 2013, adadin hujjojin da kasar Sin ta fitar zuwa Afirka ya kai dallar Amurka biliyan 92.8, adadin da ya karu da kashi 8.8 bisa dari idan aka kwatanta da na shekarar 2012, yayin da adadin hujjojin da aka shigo da su daga kasashen Afirka ya kai dallar Amurka biliyan 117.4, adadin da ya karu da kashi 3.8 bisa dari, idan aka kwatanta da na shekarar 2012. Har ila yau an bayyana cewa, yawan jarin da kamfanonin kasar Sin suka zuba a Afirka na ci gaba da karuwa. Ya zuwa yanzu dai an riga an kafa kamfanonin zuba jari a Afirka sama da dubu 2, wadanda suka shafi ayyukan noma, kayayyakin more rayuwa, sarrafawa, hakar ma'adinai, sha'anin kudi, kasuwanci da dai sauransu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China