in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya gana da ministan harkokin tsaron Amurka
2014-04-09 20:25:19 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da ministan harkokin tsaron kasar Amurka Chuck Hagel a yau Laraba 9 ga wata a nan birnin Beijing fadar gwamnatin kasar.

Yayin ganawarsu, Shugaba Xi ya bayyana cewa, ya kamata kasar Sin da kasar Amurka su kafa dangantakar aikin soja a tsakaninsu bisa ka'idojin hana aukuwar rikici, mutunta juna, hadin gwiwa da kuma cimma moriyar juna, ta yadda za a iya inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu bisa dukkan fannoni yadda ya kamata. Ya ce hakan zai iya warware sabanin dake tsakanin kasashen biyu ta hanyoyin da za su dace, kuma ya ciyar da dangantakar kasashen gaba ta hanyar da ta dace.

A nasa bangaren, Mr. Hagel ya nuna fatan cewa, za a iya ciyar da kafuwar dangantakar aikin soja ta musamman a tsakanin kasashen biyu gaba, don haka kasar Amurka na son karfafa shawarwari a tsakaninta da kasar Sin don kara fahimtar juna, ta yadda za a iya inganta dangantakar kasashen biyu, musamman ma a bangaren aikin soja tsakanin kasashen biyu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China