in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilan Sin za su halarci sabon zagaye na shawarwari kan batun nukiliyar Iran
2014-04-08 20:32:18 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya bayyana a yau Talata 8 ga wata cewa, tawagar wakilan kasar Sin dake karkashin jagorancin shugaban sashen kula da harkokin kwace damara na ma'aikatar harkokin wajen kasar Wang Qun za ta halarci shawarwari kan batun nukiliyar kasar Iran.

Taron shawarwarin da aka yi a tsakanin kasashen shida da batun nukiliyar kasar Iran ya shafa da kasar Iran zagaye na uku ya fara a birnin Vienna daga yau Talata 8 zuwa Laraba 9 ga wata, inda bangarorin da abin ya shafa za su tattauna game da yarjejeniyar batun nukiliyar kasar Iran daga dukkan fannoni.

Haka kuma Hong Lei ya yi bayani a taron manema labaran da aka yi a wannan rana cewa, kasar Sin na fatan bangarorin da abin ya shafa za su nuna fahimtar juna tare da cimma matsayi daya kan karin batutuwan da za'a tattauna a kai ta yadda za a samu ci gaba.

Ya kuma tabbatar da cewar Kasar Sin za ta ci gaba da dukufa wajen ba da taimakon da ya dace na ganin an warware batun. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China