Wakilin hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD dake kasar Cote d''Ivoire Mohamed Toure ya bayyana cewa, a halin yanzu, hukumar na dukufa wajen dawo da 'yan gudun hijirar, wadanda ke son komawa Cote d''Ivoiren. Kuma bisa kididdigar da aka yi, an ce, yawan 'yan gudun hijirar da suka riga suka koma gida daga Liberian ya kai dubu 20 a ko wace shekara. (Maryam)