in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Malaysia sun karfafa hadin gwiwar binciken jirgin saman da ya bace
2014-03-20 10:51:28 cri
Yanzu an shafe kwanaki 13 ke nan ana aikin laluben jirgin saman kasar Malaysiyan nan da ya bace. A halin yanzu, kasar Sin da kasar Malaysia sun karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu wajen binciken jirgin saman Malaysiyan da ya yi baton dabo, jiragen ruwa guda 11 na kasar Sin suna kan hanyar zuwa tekun da za su gudanar da ayyukan bincike bisa shirin da aka tsara. A sa'i daya kuma, kasashe da dama na ci gaba da aikin neman jirgin.

Wani jami'in kasar India ya bayyana a ranar Laraba 19 ga wata cewa, kasarsa ta kaddamar da sabon shirin laluben jirgin saman Malaysian nan da ya bace, cikin sabon shirin na kasar Malaysia, inda kasar ta bukaci kasar India da ta gudanar da aikin bincike a yankin kudancin tekun India. Kuma jiragen saman kasar guda biyu za su tashi daga sansanonin jihar Tamil Nadu na kudancin kasar da kuma tsibirin Andaman na kasar don gudanar da aikin ta sama.

A wannan rana kuma, shugaban kasar Amurka Barack Obama ya bayyana cewa, aikin laluben jirgin saman Malaysian ya kasance wani babban aiki ga kasar Amurka, kuma kasar na amfani da dukkan hanyoyin da take da su don taimaka wa kasar Malaysia dangane da wannan aiki. Kuma wannan shi ne karo na farko da shugaba Barack Obama ya bayyana ra'ayinsa kan wannan harka ta talebijin, tun bacewar jirgin saman na kasar Malaysia (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China