in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar sin ta kara aika jirgin saman soja a aikin neman jirgin saman kasar Malaysia
2014-03-12 20:31:20 cri
A yau ne kasar Sin ta kara aika wani jirgin saman soja baya ga wasu jiragen sama 2 da ta aika a ranar Talata don taimakawa a aikin da ake yi na neman jirgin saman kasar Malaysia da ya yi batan dabo, yayin da aka kara fadada wuraren da ake neman jirgin a halin yanzu.

A cewar kakakin rundunar soja kasar, jirgin da rundunar mayakan kasar ta aika, zai yi kokarin jiyo sautin akwatin da ke nadar bayanan jirgin a saman ruwan da ake zaton nan ne wurin da jirgin ya bace.

Dubban jiragen ruwa daga kasashe daban-daban ne suka shiga aikin gano jirgin, inda ya zuwa ranar Laraba da rana jiragen ruwan kasar Sin guda 8 ciki har da jiragen yaki 3 sun gudanar da bincike a kan ruwa ba tare da gano baraguzai ko wasu sassan jirgin ba, yayin da ake saran isowar karin jiragen ruwa.

A halin da ake ciki kuma, kasar Sin ta samar da karin taurarin dan adam guda 10 wadanda za su kara taimakawa a kimiyance a kokarin da ake yi na gano wannan jirgi samfurin Boeing 777-200, da ake saran zai sauka a Beijing da misalin karfe 6 da minti 30 na safiyar ranar Asabar da ta gabata, amma har yanzu ba a ji duriyarsa ba. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China