in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jirgin saman Malaysia da ya bace ya janyo hankulan gamayyar kasa da kasa
2014-03-11 20:47:54 cri
Yau Talata 11 ga wata da karfe shida na dare, kakakin kwamitin manyan jami'an kamfanin jiragen saman kasar ta Malaysia Ignatius ya kira wani taron manema labarai a wani otel dake birnin Beijing na kasar Sin, don yin bayani game da sabbin bayanan aikin ceton game da jirgin saman kasar Malaysia da ya bace. Ya zuwa lokacin, sa'o'i sama da 88 ke nan tun lokacin da aka daina ganin jirgin a na'urar sadarwa.

Tun lokacin da kasar Malaysia ta fitar da rahoto game da wurin da mai yiwuwa jirgin samanta kirar MH370 ya bace, ya zuwa yanzu, tawagogin aikin ceto na kasa da kasa da dama da suka hada da kasashen Sin, Malaysia, Indonesia, Vietnam, Philippines da Amurka da sauransu, sun riga sun isa wurin don dukufa wajen gudanar da aikin ceto cikin hadin gwiwa. Daga bisani kuma, kasar Japan ta bayyana cewa, za ta dukufa wajen neman jirgin sama da ya bace. A yau Talata 11 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Koriya ta Kudu Cho Teayoung ya bayyana cewa, gwamnati da jama'ar kasar suna fatan mutanen da ke cikin wannan jirgin sama za su dawo gidajensu cikin zaman lafiya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China