in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na dada fadada shiyyar binciken jirgin saman Malaysiyan da ya bace
2014-03-18 11:11:13 cri
Kwanaki 11 ke nan aka kwashe ana aikin laluben jirgin saman kasar Malaysiyan nan da ya bace,inda kasar Sin ke ci gaba da fadada shiyyar da take aikin neman wannan jirgi. A sa'i daya kuma, wasu kasashe da kungiyoyi, su ma suna ci gaba da ba da nasu taimako wajen gudanar wannan aiki.

Ya zuwa yanzu dai, yawan kasashen dake ba da tallafi wajen neman jirgin sun karu zuwa 26.

A ran 17 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya bayyana cewa, kasar Sin ta sauya shiyyar dake gudanar da aikin bincike, zuwa sauran wurare a maimakon yankunan tekun Kudancin kasar, ta kuma sha alwashin kara azamar neman jirgin yadda ya kamata.

Har wa yau a dai wannan rana ne, kakakin babban magatakardar MDD Stephane Dujarric ya bayyana cewa, a kwanan baya, kungiyar yerjejeniyar hana gwajin makaman nukiliya ta tabbatar da cewa, ba ta samun rahoton fashewa, ko faduwar jirgin saman a kasa ko a teku ba.

Da kuma karfe 8 na safiyar ranar 18 ga watan nan ne dukkan jiragen ruwan kasar ta Sin, dake jira a sashen bakin tekun kasar Thailand, suka tashi zuwa kasar Singapore, a shirin su na zuwa wasu shiyyoyi biyu dake kudu da arewaci don gudanar da aikin binciken jirgin da za a fara a nan gaba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China