in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A kalla mutane 13 sun rasu a Nijeriya a sanadiyar kifewar wani jirgin ruwa
2014-03-12 20:37:00 cri
A yau Talata 12 ga wata ne, hukumar bayar da agajin gaggawa ta Nijeriya ta tabbatar da cewa, wani jirgin ruwa ya kife a wani wurin dake kusa da birnin Lagos, wanda ya haddasa a kalla mutuwar mutane 13.

Kakakin hukumar ya bayyana wa manema labarai cewa, hadarin ya faru ne a wani tabki dake karamar hukumar Festac, inda masu aiki ceto suka ceci mutane 5, amma ya zuwa yanzu, mutane 6 sun bace.

Kakakin ya kara da cewa, dukkan mutanen dake cikin jirgin ruwan mazauna wurin ne, kuma mai iyuwa ne, daukar mutanen da ya fi karfin jirgin shi ne ya haddasa kifewarsa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China