in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ba a samu sakamako a yayin tattaunawar MDD dangane da halin da Ukraine ke ciki ba
2014-03-11 20:33:23 cri
Kafofin yada labaru na kasar Ukraine sun labarta cewa, a ranar 10 ga wata, kwamitin sulhu na MDD ya sake kiran wani taro a asirce dangane da halin da kasar Ukraine take ciki, wanda shi ne karo na 5 da kwamitin sulhu ya tattauna batun Ukraine a kwanaki kusan 10 da suka wuce. Amma a cewar Vitaly Churkin, zaunannen wakilin kasar Rasha da ke MDD, ba a tattauna wasu sabbin ra'ayoyi a yayin taron ba, don haka ba a samu sakamako a yayin taron ba.

Amma duk da haka, zaunannen wakilin kasar Faransa da ke MDD na ganin cewa, ya kamata a ci gaba da gudanar da irin wannan taro, a kokarin warware rikicin da ake fuskanta yanzu cikin ruwan sanyi.

A wannan rana, Ban Ki-moon, babban sakataren MDD ya yi kira ga gamayyar kasa da kasa da su ci gaba da kokarinsu wajen lalubo kyakkyawar hanyar warware rikicin a siyasance cikin dogon lokaci, da kuma taimakawa Ukraine wajen sassauta zaman dar-dar a kasar.

A wata sabuwa kuma, a ranar 13 ga wata, Arseniy Yatseniuk, firaministan Ukraine na wucin gadi zai yi jawabi a taron kwamitin sulhu, inda zai yi karin bayani kan halin da kasarsa ke ciki. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China