in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar bayar da agaji ta Red Cross ta yi allah wadai da kisan ma'aikatanta dake Afirka ta Tsakiya
2014-03-09 17:30:06 cri
Hukumar bayar da agaji ta Red Cross mai hedkwata a birnin Geneva ta ba da wata sanarwa, inda ta yi allah wadai da yadda wasu dakarun da ba a san asalinsu ba suka kashe ma'aikatan da hukumar ta yi hayarsu a jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.

Sanarwar ta bayyana cewa, wasu dakaru ne suka shiga gidajen ma'aikatan hukumar a birnin Ndele dake arewacin kasar Afirka ta Tsakiya, a lokacin, akwai ma'aikata hudu a cikin gidajen, inda dakarun suka kashe daya dake cikinsu, kana guda ukun suka tsira da rayukansu.

Wakilin hukumar dake jamhuriyar kasar Afrirka ta Tsakiya ya yi allah wadai da lamarin. Ya kuma yi kira da bangarorin da abin ya shafa a kasar Afirka ta Tsakiya da su kiyaye dokokin kasa da kasa yadda ya kamata, don ba da tabbaci ga ayyukan ma'aikatan jin kai.

A kwanan baya, yanayin tsaro ya tabarbare a kasar Afrika ta Tsakiya sakamakon fadace-fadacen ke kawo cikas ga ayyukan taimakon jin kai ga jama'ar kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China