in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin a MDD ya jaddada muhimmancin yaki da talauci a shirin cimma muradun karni bayan 2015
2014-02-27 10:48:04 cri

Mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Wang Min, ya ce, wajibi ne a sanya batun yaki da talauci a sahun gaba, cikin jerin kudirorin cimma muradun karni ko MGDs bayan shekarar 2015.

Mr. Wang ya bayyana hakan ne a ranar Laraba, yayin taron majalissar tattauna batutuwan tattalin arziki da zamantakewa, da suka shafi shirye-shiryen samar da ci gaba na shekarar 2014.

Wakilin na kasar Sin ya ce, yaki da fatara, na cikin manyan kalubale da duniya ke fuskanta, kuma aiki ne da ya wajaba a sanya gaba, muddin dai ana burin samar da ci gaba mai dorewa.

Da yake tsokaci kan kudurin shirin cimma muradun karni na tabbatar da ci gaban daukacin sassan duniya, Mr. Wang ya ce, a ko da yaushe kasar Sin na baiwa shirin na MDGs cikakken goyon baya, ta hanyar ba da tata gudummawa ga shirye-shiryen wanzar da ci gaba.

Ana dai fatan sabon shirin na MDGs wanda za a aiwatar bayan shekarar 2015, zai maye gurbin kudurorin nan 8, da ake burin kammalar su nan da shekarar ta 2015. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China