Sin ta kasance gaba kan karbar rokon mallakar fasaha cikin shekaru 3 da suka gabata
Bisa labarin da hukumar kula da ikon mallakar ilmi ta kasar Sin ta fitar a yau Alhamis 20 ga wata, a shekarar 2013 da ta gabata, hukumar ta karba jimillar adadin rokon mallakar fasaha har dubu 825, adadin ya karu da kashi 26.3 bisa dari, idan aka kwatanta da na shekarar 2012.
Wannan adadi ya sanya kasar ta Sin kasance a sahun gaba a wannan fanni, cikin jimillar kasashen duniya a tsakanin shekaru uku da suka gabata.
Bugu da kari, kasar ta Sin ta ba da iznin lambar kira ta fasaha da yawansu ya kai dubu 208, ciki hada da dubu 144 da suka jibanci lambar kira ta fasahar cikin gida, adadin ya yi daidai da na shekarar 2012. (Maryam)