in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Sin ta kebe kudaden da yawansu ya kai RMB biliyan 20.7 don kyautata yanayin karatu a kauyuka
2013-12-12 16:58:27 cri
A ranar 11 ga wata, ma'aikatar kula da harkokin kudi ta kasar Sin ta bayar da labari cewa, ya zuwa yanzu, gwamnatin kasar Sin ta riga ta kebe kudaden da yawansu ya kai kudin Sin RMB biliyan 20.7 a shekarar bana, domin kyautata yanayin karatu a kauyuka.

A shekarar 2010, kasar Sin ta gudanar da shirin kyautata makarantu ta hanyar tilastawa bada ilmi a kauyuka, da kokarin kawar da matsalolin da suke kawo tarnanakaki wajen raya sha'anin ilmi a kauyuka, haka kuma za a cigaba da kokari wajen raya kayayyakin koyarwa, da gyara makarantu.

Bisa kididdigar da aka yi, an ce, daga shekarar 2010 zuwa shekarar 2013, gwamnatin tsakiya ta kasar Sin ta riga ta ba da kudaden agaji da yawansu ya kai kudin Sin RMB biliyan 65.68 domin taimakawa raya fannin ilmin kasar baki daya.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China