in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar EU za ta dage takunkumin da ta kakaba wa wasu manyan jami'an Zimbabwe
2014-02-20 11:04:12 cri
Darektan kula da harkokin yankunan kudanci da gabashin Afirka da tekun India na kungiyar tarayyar kasashen Turai Koen Vervaeke ya bayyana a birnin Harare, babban birnin kasar Zimbabwe cewa, kungiyar EU ta tsai da kudurin dage takunkumin da ta kakaba wa manyan jami'an jam'iyyar dake mulkin a kasar Zimbabwe, amma ban da shugaban kasar Robert Mugabe da kuma uwargidansa.

A yayin taron manema labaran da aka yi a wannan rana, Mr. Vervaeke ya bayyana cewa, kungiyar ta tsai da kudurin ne bisa hujjar cewa, cikin 'yan shekarun nan, kasar Zimbabwe ta taka rawar gani wajen yin kwaskwarima a fannin demokuradiyya, amma kungiyar ba ta kawar da dukkan takunkumin da ta kakaba wa manyan jami'an kasar Zimbabwe ba, domin tana tsammanin cewa, kasar na da damar kara kyautata yanayin dimokuradiyya a kasa. Bugu da kari, takunkumin da kungiyar EU ta kakaba wa wadannan manyan jami'ai sun hada da hana su shiga kasashen kungiyar EU, da bude asusun ajiya a bankunan kasashen kungiyar.

Cikin shekaru da dama da suka gabata ne, kasar Amurka da kungiyar EU suka kakaba wa kasar Zimbabwe wasu takunkumin da suka hada da hana jigilar makamai da dai sauransu, da nufin sanya wa kamfamoni mallakar jam'iyyar dake mulkin kasar Zimbabwe takunkumi.

Cikin watan Disamban shekarar da ta wuce, yayin da ya ke rantsar da sabbin mambobin majalisar ministocin kasar, shugaba Mugabe ya bayyana cewa, kasar Zimbabwe ba ta tsaron takunkumin da yammacin kasashen suka kakaba mata, kana za ta fuskance su ta hanyar karfafa hadin gwiwa tare da kasashen muhimman abokanta a fannin tattalin arziki da cinikkaya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China