in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zimbabwe ta kara karfin ikon mallakar masana'antu ga 'yan kasarta
2014-01-02 15:16:31 cri
Tun daga ranar 1 ga watan Janairun sabuwar shekara, gwamnatin Zimbabwe ta fara kara karfin ikon mallakar masana'antu ga 'yan kasarta, inda ta bukaci masana'antu na kasashen waje a fannin shuke-shuken amfanin gona, sayar da kayayyaki, da masu yin aski da su mika hannun jari da kashi 51 cikin 100 ga 'yan kasarta.

Bisa umurnin da ma'aikatar kula da harkokin matasa da ba da kariya ga tattalin arziki na Zimbabwe ta bayar, an ce, dole ne 'yan kasashen waje da suka gudanar da sana'o'i 14 a kasar, cikinsu har da sayar da kayayyaki bisa kansu, da zirga-zirga, da shuke-shuken amfanin gona, da kaddarorin gidaje, da yin taba, da madara, su mika ikon mallakar masana'antunsu ga 'yan kasar kafin ranar 1 ga wata, idan ba a dauki wannan mataki ba, za a keta dokar kasar.

Kwanan baya, ministan kula da harkokin matasa, da ba da kariya ga tattalin arzikin kasar Francis Nhema ya bayyana cewa, za a aiwatar da wannan doka har na tsawon shekaru 4 zuwa 5, kuma gwamnatin Zimbabwe ta amince da 'yan kasar da su nemi abokan ciniki daga kasashen waje, amma dole ne su tabbatar da samu yawancin hannun jarin masa'anatu. A sa'i daya kuma, tun daga ranar 1 ga watan Janairu na bana, yayin da Zaimbabwe ta ba da lasisin gudanar da ayyuka a sana'o'i da Zimbabwe ta ba da kariya a kai, za ta bayar da su ga 'yan kasar Zimbabwe a farko.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China