in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana fatan Amurka za ta iya daidaita manufofinta dake shafar yankin Asiya da Pacific bisa bukatun yankin
2014-02-08 20:41:37 cri
A 'yan kwanakin baya ne,wani jami'in gwamnatin kasar Amurka mai lura da harkokin yankunan Asiya da Pacific, ya yi bayani game da manufofin kasarsa a wannan shekara ta 2014 wadanda suke shafar yankunan biyu.

Jami'in ya ce kasar Amurka za ta ci gaba da gudanar da manufarta ta girke jiragen ruwan yakin kasa kimanin kashi 60 bisa dari a yankin Pacific kafin shekarar 2020, tare da kara karfinta a fannonin tattalin arziki, tsaro, kiyaye muhalli, inganta mu'amala da zaman takewar al'umma, raya dimokuradiyya a yankunan da dai sauransu.

Don gane da wannan batu, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya bayyana a yau Asabar 8 ga wata cewa, kiyaye zaman lafiyar wadannan yankuna, da bunkasar tattalin arzikin yankunan, da kuma zurfafa hadin gwiwar dake tsakanin kasashen yankunan sun dace da moriyar kasashen yankunan Asiya da Pacific.

Ya ce kasar Sin na fatan Amurka za ta iya daidaita manufofinta bisa bukatun kasashen yankunan, ta yadda za ta ba da gudumawa wajen kiyaye zaman lafiya, da lumana da kuma bunkasuwar yankunan Asiya da Pacific. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China